in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar zaben kasar Ghana ta bada gurabe ga jam'iyyu a zaben majalisun dokokin kasar
2016-10-21 10:31:27 cri
Hukumar zaben kasar Ghana (EC) ta baiwa jam'iyyun siyasar kasar wurare a jikin kuri'un zabukan majalisar dokokin kasar da za'a gudanar a watan Disamba.

Baki daya, wakilan jam'iyyun siyasa 7 ne suka zabarwa 'yan takarkarunsu gurabe a jikin kuri'un.

Jam'iyyar GCPP ce ta farko a jikin kuri'ar, sai PPP dake bi mata, sai kuma jam'iyyar NDC mai mulkin kasar.

Wannan ne karon farko da hukumar zaben kasar ta Ghana ta bada dama ga jam'iyyun kasar don zabar gurabe a jikin kuri'un da za'a kada a zaben kasar.

A watan Disamba ne al'ummar kasar Ghana za su fita rumfunan zabe, domin zabar shugaban kasa da mambobin majalisar dokokin kasar su 275.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China