Shugabar hukumar zartarwar kungiyar Madam Nkosazana Dlimini Zuma wadda ta bayyana hakan cikin wata sanarwar da aka rabawa manema labarai a jiya Alhamis, ta bayyana cewa, daukar wannan mataki ya biyo bayan gayyatar da gwamnatin kasar ta Ghana ta mikawa kungiyar ce.
Sanarwar ta ce, ana saran tura tawagar ce a ranar 20 ga watan Oktoba, kuma za ta kasance a kasar har zuwa lokacin da za a sanar da sakamakon karshe na zabukan kasar.(Ibrahim)