in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi taron karawa juna sani kan harkokin jam'iyyun siyasa a tsakanin Sin da Afirka karo na 2 a birnin Chongqing na Sin
2016-10-15 13:22:05 cri
Jiya Jumma'a aka gudanar da taron karawa juna sani kan harkokin jam'iyyun siyasa a tsakanin Sin da Afirka karo na 2 a birnin Chongqing na kasar Sin.

Shugaban hukumar kula da harkokin yin cudanya da jami'yyun siyasa na kasashen ketare na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin Song Tao, ya halarci bikin bude taron, inda ya bayyana cewa, ya kamata jam'iyyun kasar Sin da kasashen Afirka su nuna kwazo wajen neman hanyoyin bunkasuwa, da kuma inganta harkokin yin shawarwari kan fasahohin neman cigaba a tsakanin Sin da Afirka, ta yadda za a ciyar da hadin gwiwar Sin da Afirka gaba.

Kaza lika, jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin tana son habaka sabbin hanyoyin yin shawarwari da mu'amala bisa fannonin daban daban a tsakanin bangarori daban daban da abin ya shafa, haka kuma, ana son zurfafa shawarwarin dake tsakanin jam'iyyun kasar Sin da kasashen Afirka ta hanyar yin taron karawa juna sani kan harkokin jam'iyyun siyasa a tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China