in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An shiga wani sabon mataki na yin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka
2016-09-09 11:12:45 cri
A jiya Alhamis 8 ga wata, an rufe taron dandalin tattaunawar zuba jari ga kasashen Afirka karo na biyu na tsawon kwanaki biyu. A gun babban taron, kamfanonin Sin da na kasashen Afirka sun daddale jerin yarjeniyoyin dake shafar fannonin zirga-zirgar jiragen sama , da samar da wutar lantarki, da sha'anin kere-kere da sauransu, wadanda darajarsu ta kai sama da dala biliyan 2.5.

Mataimakin darektan kwamitin kula da harkokin bunkasuwa da yin kwaskwarima na Sin, Ning Jizhe ya bayyana cewa, kawo yanzu baki daya jimillar jarin da Sin ta zuba a kasashen Afirka ta kai sama da dala biliyan 100, a yayin da kamfanonin Sin sama da 3100 suna zuba jari tare da gudanar da harkokinsu a kasashen Afirka. Bisa sakamakon da aka samu a taron koli na Johannesburg, hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu a fannin masana'antu ya riga ya zama babban karfi na bunkasa masana'antun Afirka.

Shugaban hukumar sa kaimi ga zuba jari da fitar da kayayyaki zuwa ketare ta kasar Saliyo ya bayyana cewa, yadda kamfanonin Sin suke zuba jari ga kasashen Afirka ba ma kawai zai taimaka wa kasashen Afirka wajen kyautata karfin masa'anatunsu ba, har ma zai rarraba fasahohin kamfanonin Sin zuwa ga kasashen Afirka, ta yadda za su tabbatar da kirkire-kirkire.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China