Xi Jinping zai kai ziyara Cambodia, Bangladesh da Indiya
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya sanar a yau Litinin 10 ga wata cewa, bisa gayyatar sarkin kasar Cambodia Norodom Sihamoni, shugaban kasar Bangladesh Abdulla Hameed, firaministan kasar Indiya Narendra Modi suka yi masa, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai kai ziyara kasashen Cambodia da Bangladesh tun daga ranar 13 zuwa 17 ga wannan wata, tare da halartar taron ganawar shugabannin kasashen kungiyar BRICS karo na 8 da za a yi a birnin Goa dake kasar Indiya. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku