in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya gana da 'yan wasan kasar Sin wadanda suka halarci gasar wasannin Olympics ta Rio
2016-08-25 20:25:26 cri

A yau Alhamis da yamma, shugaban kasar Sin Xi Jinping da sauran manyan shugabannin kasar suka gana da tawagar 'yan wasan kasar da jami'ansu wadanda suka halarci gasar wasannin motsa jiki ta Olymics karo na 31 da aka kammala a Rio, inda ya yi musu maraba da dawo tare da ya nuna yabo da taya su murnar samun nasara a yayin gasar.

Xi Jinping ya jaddada cewa, 'yan wasannin motsa jiki na kasar Sin sun yi namijin kokari kuma sun samu nasara sosai a yayin gasar wasan Olympics ta Rio, sun kuma nuna ruhun Olympics da ruhun al'ummar Sinawa a yayin da suke fafatawa a gasar.

Xi Jinping ya kuma nuna cewa, bunkasuwar wasannin motsa jiki wata muhimmiyar alama ce dake bayyana yadda ake bunkasa zaman al'umma da ci gaban bil Adama, kuma muhimmiyar alama ce dake nuna karfin kasa. Yana fatan za a yi kokarin samun nasarar shirya gasar wasan Olympics ta lokacin sanyi da za a yi a nan Beijing a shekarar 2022 domin ci gaba da bunkasa wasannin motsa jiki a kasar. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China