in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya zata kawo karshen cutar Maleriya nan da shekarar 2020
2016-10-08 13:18:11 cri
Gwamnatin Najeriya tace tana yunkurin bullo da wani tsari wanda ake saran zai kawo karshen cutar zazzabin cizon sauro a fadin kasar kafin nan da shekarar 2020.

Shekaru da dama da suka wuce, an sha gabatar da matakan yaki da cutar ta Maleriya a matakai na kasa da kasa a Najeriyar, to sai dai a wannan karo, gwamnatin ta ce matakan da take shirin dauka za su kawar da cutar ne kwacokan a fadin kasar.

Gwamnatin Najeriyar tace, ta bullo da shirin kawar da cutar Maleriyar wanda aka tsara shi ta yadda kwayoyin cutar ba za su taba yin tasiri ba a jikin bil adama a duk fadin kasar.

A cewar Patricia Uhomoibhi, babban jami'i a ma'aikatar lafiya ta kasar, dabarun da aka bullo dasu zasu maida hankali ne, wajen daukar matakan farko da kawar da cutar nan da sheklara ta 2020, da kuma kawo karshen hasarar rayukan da ake samu a sanadiyyar cutar nan da shekarar ta 2020.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China