in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan bindiga sun sace tsohuwar minista a Najeriya
2016-10-05 11:54:42 cri
Rundunar 'yan sanda a Najeriya ta bayyana a jiya Talata cewa, wasu 'yan bindiga da ba a tantance su ba, sun yi awon gaba da tsohuwar ministar kula da muhalli Lawrencia Laraba-Mallam da mijinta Pius ranar Litinin da yamma a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna.

Kakakin rundunar 'yan sandan jihar Kaduna Aliyu Usman wanda ya tabbatar da hakan ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin, ya ce, 'yan bindigar ba su taba direban nasu ba. Ya ce, jami'ansu na daukar dukkan matakan da suka wajaba don tabbatar da cewa,an kubutar da mutanen biyu.

A halin da ake ciki yanzu,'yan bindigar sun tuntubi iyalan ministar, inda suka bukaci a ba su naira miliyan 10 kimanin dala 32,000 a matsayin kudin fansa kafin su saki ministar da kuma mijin nata.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China