in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Buhari zai yiwa 'yan majalissun dokoki bayani game da yanayin tattalin arzikin Najeriya
2016-10-07 12:25:55 cri
Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya, zai yiwa mambobin majalissun dokokin kasar karin haske, game da matakan da gwamnatin sa ke dauka, don farfado da tattalin arzikin kasa, da kuma tsamo kasar daga mawuyacin halin da take ciki. Majalissar dattawan kasar ce dai ta tabbatar da shirin ganawar, ko da yake ba ta tabbatar da rana ko lokaci ba.

Tun dai bayan kammala hutun su a kwanan baya, 'yan majalissun dokokin Najeriyar ke daukar matakan da suke fatan za su tallafa, wajen fidda kasar daga halin koma bayan tattalin arziki da take fama da shi. Tuni kuma 'yan majalisar dattijan Najeriyar suka bayyana aniyar gudanar da wani taro na yini biyu domin tattauna wannan matsala.

Tattalin arzikin Najeriya ya fada mawuyacin hali a hukunce, tun bayan da ma'aunin GDPn kasar ya yi kasa da kaso 2.06 bisa dari, a watanni 3 na biyu na shekarar bana, bayan da GDPn na yi kasa da kaso 0.36 a watanni 3 na farkon shekarar.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China