in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar kiyaye muhalli ta MDD ta godewa Sin bisa ga muhimmiyar rawar da ta taka wajen taimakawa ga cimma yarjejeniyar Paris
2016-10-07 12:40:27 cri
A yayin da ake shirin fara aiwatar da yarjejeniyar tinkarar sauyin yanayi ta birnin Paris a ranar 4 ga watan Nuwanba. Shugaban gudanarwa na hukumar kiyaye muhalli ta MDD Erik Solheim ya bayyanawa 'yan jarida a kwanakin baya cewa, yana godiya ga kasar Sin bisa ga muhimmiyar rawar da ta taka a kokarin ganin an cimma yarjejeniyar Paris, da taka rawar a zo a gani a fannin kiyaye muhalli a duniya.

Mr Solheim ya bayyana cewa, a watan Satumban bana ne, manyan kasashe masu karfin tattalin arziki a duniya, da suka hada da Sin da Amurka suka amince da yarjejeniyar ta Paris, wannan ya taimaka wajen fara aiwatar da yarjejeniyar. A cewarsa, kasar Sin tana kokarin daukar matakai ba tare da gurbata yanayi ba wajen magance matsalar sauyin yanayi da gurbata muhalli, da taimakawa wajen samar da ayyukan yi da samun bunkasuwar tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba, wannan mataki ne da ya kamata sauran kasashen duniya su yi koyi.

Mr Solheim ya ce, kasar Sin ta yi kira da aiwatar da tsarin hadin gwiwar dake tsakanin kasashe masu tasowa, da samar da gudummawa da yada fasahohi, da samar da fasahohi ga yankin Afirka dake kudu da hamadar Sahara da kasashe masu tasowa dake dab da yankin. Yana fatan kasar Sin za ta kara taimakawa yaduwar fasahohin samun bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China