in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a yi bikin mikawa da ajiye yarjejeniyar Paris a watan Satumba
2016-07-20 10:33:19 cri
Mataimakin kakakin babban sakataren MDD Farhan Haq ya bayyana a jiya Talata cewa, MDD za ta yi bikin mikawa da ajiye yarjejeniyar Paris a ranar 21 ga watan Satumba ta yadda za a hanzarta fara aiwatar da yarjejeniyar tinkarar sauyin yanayin duniya da aka cimma.

Haq ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a wannan rana cewa, yanzu haka babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya gayyaci shugabannin kasa da kasa da su halarci bikin amincewa ko karba ko kuma shiga yarjejeniyar ta Paris. A cikin wasikar gayyatar, Ban Ki-moon ya yi kira ga kasashen duniya da su gaggauta kammala matakan amincewa da yarjejeniyar Paris din kafin karshen wannan shekara.

Haq ya bayyana cewa, wannan bikin zai baiwa sauran kasashen duniya damar shiga ko amincewa da yarjejeniyar ta Paris kafin karshen shekarar bana.

Ya zuwa yanzu, kasashe 19 ne suka kammala matakin amincewa ko shiga wannan yarjejeniya. Wasu kasashe ciki har da Sin da Amurka sun bayyana aniyarsu ta shiga yarjejeniyar kafin karshen wannan shekara. Sin za ta kammala dukkan matakan shiga yarjejeniyar kafin a gudanar da taron kolin kungiyar G20 da za a gudanar a birnin Hanzhou na kasar Sin a watan Satumba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China