in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kashe sojoji a kalla 22 a Nijar
2016-10-07 12:13:44 cri
Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na cewa, wasu 'yan bindiga da ba a tantance su ba, sun kashe a kalla sojojin kasar 22 a wani harin da suka kai a wani sansanin 'yan gudun hijra da ke Tassara a yammacin kasar a jiya Alhamis.

Wata majiya ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin cewa, 'yan bindigan sun kaiwa sojojin Nijar da ke gadin sansanin 'yan gudun hijira galibinsu 'yan kasar Mali hari, inda suka kashe a kalla sojoji 22. Majiyar ta ce,ana zaton masu kaifin kishin Islama daga yankin arewacin kasar Mali ne suka kai wannan hari.

Sai dai mahukuntan Nijar ba su ce komai ba game da wannan hari, amma yanzu haka, sojojin Nijar sun baza komarsu don farautar maharan.

Gidan talabijin na kasar Nijar ya ba da rahoto a jiya Alhamis da dare cewa, wasu 'yan bindiga sun kaiwa sansanin 'yan gudun hijira da ke yammacin kasar hari. Yana mai cewa, mutane da dama sun jikkata,amma bai fayyace adadin wadanda suka jikkatan ba.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China