in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An damke jagoran 'yan adawa a kasar Zambia
2016-10-06 12:02:35 cri
Rundunar 'yan sandan kasar Zambia ta damke jagoran babbar jam'iyyar adawar kasar ta UPND Hakainde Hichilema, da mataimakin sa Geoffrey Mwamba, bisa zargin su da furta kalamai da ka iya rura wutar rikici.

An dai tsare mutanen biyu ne a ranar Laraba, bayan 'yan sanda sun gayyace su wata tattaunawa a garin Luanshya dake lardin Copperbelt cikin makon da ya gabata.

'Yan sandan sun bukaci mutanen biyu su bada bahasi game da kalaman da suka furta, yayin da suka ziyarci wasu 'yan jam'iyyar su dake tsare a garin na Luanshya tun bayan babban zaben kasar na watan Agusta.

Kwamishinan 'yan sandan Copperbelt Charity Katanga ya tabbatar da tsare mutanen biyu, bisa zargin yunkurin tunzura magoya bayan su, cikin wani jawabi da suka gudanar a ranar 26 ga watan Satumbar da ya gabata.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China