in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gudanar da taron kungiyar AU game da tsaron tekuna a Togo
2016-10-05 16:33:40 cri
Kungiyar hadin kan nahiyar Afirka ta AU, za ta gudanar da taro game da matsalolin tsaro a ruwayen nahiyar, taron da zai gudana mako mai zuwa a birnin Lome na kasar Togo.

Da yake tabbatar da hakan a ranar Litinin, ministan wajen kasar Togo Robert Dussey, ya ce za a gudanar da taron ne tsakanin ranekun 10 zuwa 15 ga watan nan, da nufin zakulo hanyoyin magance kalubalen tsaro a tekunan Afirka, da matsalar su ba bisa ka'ida ba, tare da tabbatar da kare nagartar ruwayen nahiyar.

Ana sa ran shuwagabannin nahiyar kimanin 25 zuwa 30 ne za su hallara, cikin jimillar wakilai 3,000 da ake fatan isar su taron.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China