in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin kasar Sin za su shiga aikin yaki da 'yan fashin teku a yankin tekun Guinea
2016-07-29 19:07:22 cri
Tsohon shugaban ofishin kula da harkokin kasashen waje na ma'aikatar harkokin tsaron kasar Sin Qian Lihua ya bayyana cewa, sojojin kasar Sin za su taimakawa kasashen yammacin Afirka wajen tabbatar da tsaron zirga-zirgar jiragen ruwa a yankin tekun Guinea, a daidai lokacin da yankin ya ke fama da karuwar barazanar 'yan fashin teku.

Qian Lihua ya bayyana hakan ne yayin taron tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Afirka wanda ke gudana a birnin Lome. Ya kuma gabatar da wasu shawarwari kan yadda za a yaki 'yan fashi teku a yankin tekun Guinea.

Bugu da kari, ya ce kasar Sin za ta shiga a dama da ita a kokarin da kasashen duniya suke yi na yaki da 'yan fashin teku a yankin tekun Guinea, ta hanyar taimakawa kasashen da ke shiyyar wajen gina wasu muhimmman kayayyakin more.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China