in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kenya ta karyata zargin aikata kisan gilla
2016-10-05 12:14:11 cri
Babban sakatare a ma'aikatar cikin gidan kasar Kenya Joseph Nkaissery, ya karyata zargin da ake yiwa 'yan sandan kasar da aikata kisan gilla.

Mr. Nkaissery ya yi watsi da zargin da wasu kafofin watsa labaran kasar ke yadawa ne a jiya Talata, yayin wani taron 'yan jaridu, yana mai cewa kafofin na yada wannan bayanai ne da wata mummunar manufa.

Kalaman nasa na zuwa ne bayan da wata jaridar kasar ta fidda wani rahoto dake cewa tsakanin watan Janairu zuwa Agustan bana, 'yan sandan kasar ta Kenya sun hallaka fararen hula 121. Kaza lika daga shekarar bara zuwa yanzu, 'yan sandan sun kashe mutane da yawan su ya kai 262 ba tare da gurfanar da su a gaban kuliya ba.

Mr. Nkaissery ya kara da cewa, a matsayin kasa mai bin doka da oda, babu yadda za a yi 'yan sandan Kenya su rika hallaka mutane ba tare da wani dalili na shari'a ba. Ya ce wannan alkaluma da jaridar ta fitar, ba za su tabbatar da zargin da ake yiwa 'yan sandan kasar na aikata kisan gilla ba.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China