in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Layin dogo da Sin ta gina a Kenya ya zama abin misali ga hadin gwiwa tsakanin Sin da Afrika
2016-08-17 11:14:31 cri
A jiya Talata ne, ofishin jakadancin kasar Sin dake kasar Kenya ya gayyaci jakadun kasashen Afrika dake Kenya fiye da 10 don su ziyarci wurin da ake aikin gina layin dogo tsakanin Mambasa da Nairobi wanda kamfanin Sin ke daukar nauyin gina shi.

Jami'an diflomasiyar sun nuna cewa, ba mai kawai wannan layin dogon zai taimaka wajen raya tattalin arzikin kasar Kenya ba, hatta ma zai ciyar da tattalin arzikin sauran kasashe dake gabashin Afrika gaba. Haka kuma yana da muhimmanci sosai wajen cimma burin muradun nahiyar Afrika na shekarar 2063 da tabbatar da sakamakon da aka samu a taron kolin dandanlin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afrika(FOCAC) da aka yi a Johnnesberg na kasar Afirka ta kudu

Ban da wannan kuma, an yi hasashen cewa, wannan layin dogo zai taimakawa ci gaban GDPn kasar Kenya da kashi 1.5 bisa dari, da kuma ciyar da tattalin arziki da sauran fannonin rayuwa gaba, da sa kaimi ga cinikayyar shige da fice ta kasar Kenya. Haka kuma aikin gina layin dogon ya samar da guraben aikin yi fiye da dubu 30, matakin da ya taimaka wajen warware matsalar rashin aikin yi da ake fama da ita a wurin. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China