in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya sun saki mutane 348 da aka zarge su da kasancewa 'yan Boko Haram
2016-10-02 13:17:47 cri
Sojojin kasar Najeriya sun saki wasu mutane 348 da aka zarge su da kasancewa 'yan Boko Haram bayan da aka wanke su daga tuhumar da ake musu na aikata laifi, a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar, a cewar wani hafsan sojin kasar a ranar Asabar.

Hafsan sojin wato birgadiya janar Victor Ezugwu, ya ce, da ma an kama wadannan mutane a yayin da sojoji suke gudanar da ayyukansu daban daban na murkushe 'yan ta'adda a jihar Borno. Cikin mutanen, akwai maza 114, da mata 107, gami da yara 127, a cewar hafsan.

Ezugwu ya kara da cewa an riga an mika mutanen ga Kashim Shettima, gwamnan jihar Borno, yayin wani bikin da aka gudanar da Maiduguri, hedkwatar jihar. Kafin hakan, a cewar hafsan, an yi wa mutanen tambayoyi don tabbatar da cewa ba su da wata alaka da kungiyar Boko Haram.

Kuma daga karshe an tabbatar da cewa wadannan mutane ba su da wani laifi, shi ya sa aka yanke shawarar sakin su nan take, domin su koma zaman rayuwarsu yadda ya kamata bisa 'yanci da dokokin kasa.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China