in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bude wani bincike kan matsalar jin kai a Burundi
2016-10-01 12:05:27 cri
Kwamitin kare 'yancin dan adam na MDD ya dauki niyya a ranar Jumma'a na kafa wani kwamitin da zai tafiyar da wani bincike mai zurfi kan tauye tauyen hakkin dan adam da aka aikata a kasar Burundi tun a shekarar 2015.

A cewar wani kudurin da aka cimma da kuri'u 19 na amincewa da kuri'u 7 na kin amincewa kana da kuri'in janye jiki 21, wannan kwamitin bincike zai kula da tantance mutanen da aka zarge da tauye tauyen hakkin dan adam da aka aikata a cikin kasar, da tsara wasu shawarwari kan matakan da za a dauka domin tabbatar da cewa wadannan mutane sun amsa laifinsu gaban kuliya, duk da matsayin da suke da ko wani goyon baya, da kuma tattaunawa tare da hukumomin Burundi da dukkan bangarori daban daban masu ruwa da tsaki ta yadda da za a samar da tallafi da shawarwarin da suka wajaba wajen kyautata nan take matsalar 'yancin dan adam da kuma yaki da rashin hukunci, in ji MDD a cikin wata sanarwa.

Haka kuma,kwamitin 'yancin dan adam din ya bukaci gwamnatin Burundi da ta bada hadin kai yadda ya kamata ga kwamitin binciken, da bada umurnin kai ziyara a cikin kasar da kuma samar da dukkan bayanan da ake bukata wajen tafiyar da aikin tawagar binciken, in ji sanarwar. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China