in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan kasar Burundi na yin zanga zangar adawa da MDD game da tura dakaru zuwa kasar
2016-07-31 12:11:20 cri
Dubun dubatar al'ummar kasar Burundi na gudanar da zanga zanga a kasar domin nuna bacin ransu ga matakin da kwamitin tsaron MDD ya dauka na tura jami'an 'yan sanda kimanin 228 domin aikin tabbatar da tsaro a kasar.

An dai gudanar da zanga zangar ne a manyan titunan Bujunbura, babban birnin kasar, domin nuna bacin ransu game da abin da suka kira Faransa tana tsokanarsu, saboda gabatar da kuduri a gaban kwamitin sulhu na MDD na neman tura dakaru zuwa kasar.

Dubban 'yan kasar sun taro a ofishin jakadancin Faransa dake kasar, inda suke bayyana cewa ba za su amince 'yan kasashe waje su shiga Burundi ba muddin suna raye, kuma ba za su amince Faransa ta zaba musu shugaban kasa ba.

Da yake tsokaci, magajin garin Bujunbura Freddy Mbonimpa ya ce, daga cikin makasudin zanga zanagar shi ne domin nunawa kafafen yada labaru na cikin gida da na kasashen waje cewa, kasar Burundi tana zaune lafiya, kuma tana da 'yancin kanta, kana ba ta bukatar a turo mata wasu dakaru daga kasashen waje, kuma suna bukatar Faransa da ta dakatar da tsokanar da take yiwa kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China