in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNHCR: 'Yan gudun hijira daga Burundi sama da dubu 300 sun gudu zuwa kasashe makwabta
2016-09-24 12:24:37 cri
A jiya Jumma'a 23 ga wata, hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD (UNHCR) ta bayyana cewa, tun bayan barkewar rikici a Burundi a watan Afrilun bara zuwa yanzu, 'yan gudun hijira sama da dubu 300 daga kasar sama da dubu 300 sun tsere zuwa kasashe makwabta domin neman mafaka.

A wannan rana hukumar UNHCR ta ba da sanarwa a birnin Kampala cewa, 'yan gudun hijira na Burundi sun gudu zuwa Tanzaniya da Ruwanda da Uganda da Kongo Kinshasa da kuma Zambiya sakamakon barkewar tashe tashen hankali, barazana, yin garkuwa da sace mutane da sauransu.

Hukumar ta bayyana cewa, sabo da karancin karfi na wasu kasashen dake karbar 'yan gudun hijira, 'yan gudun hijira na Burundi da dama, musamman ma mata da yara, suna cikin mawuyacin hali.

Sanarwar ta kara da cewa, domin ba da kariya ga 'yan gudun hijira, hukumar UNHCR ta yi kira ga kasa da kasa da su yi kokarin tabbatar da zaman lafiya, tare da kara nuna goyon baya ga wadannan kasashe masu karbar 'yan gudun hijira.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China