in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
ICGLR zai daidaita sabanin dake tsakanin Burundi da Rwanda
2016-09-15 13:03:05 cri
Mai magana da yawun shugaban kasar Burundi ya fada cewa, babban taron kasa da kasa game da manyan tekuna (ICGLR) ya sha alwashin daidaita rashin fahimtar juna dake wanzuwa tsakanin kasashen Burundi da Rwanda.

Sanarwar ta zo ne bayan wata ziyarar da jami'an ICGLR suka kaiwa sabon babban sakataren shugaba Pierre Nkurunziza na kasar Burundi, Zachary Muburi Muita.

Dangantaka ta fara tsami ne tsakanin kasashen Burundi da Rwanda, tun a watan Afrilun shekarar 2015, a lokacin da shugaban kasar Burundin Pierre Nkurunziza, ya yanke shawarar neman wa'adin shugabancin kasar a karo na 3, lamarin da ya saba da dokokin kundin tsarin mulkin kasar, da kuma batun yarjejeniyar Arusha ta 2000.

An zargi kasar Rwanda da laifin ba da mafaka ga 'yan kasar Burundi wadanda suka yi yunkurin shirya juyin mulki a ranar 13 ga watan Mayun shekarar 2015, sannan an zarge ta da ba da horo na soji ga wasu mutane da nufin ta da hankalin kasar Burundin.

Sai dai Rwanda ta sha musanta zarge zargen da ake yi mata. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China