in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ba a yi zaben majalisar wakilai a Somaliya a lokacin da aka tsara ba
2016-09-26 10:23:51 cri
A yanzu haka, hukumar zaben tarayyar kasar Somaliya da hukumomin zabe na gwamnatocin jihohin kasar suna ci gaba da yin shawarwari don warware wasu matsaloli, a sakamakon tsaikon da aka samu game da gudanar da zaben majalisar wakilai da kuma majalisar dattijai a kasar Somaliya a ranar 24 da ranar 25 ga watan nan da muke ciki. Don haka za a gudanar da zabukan 2 ba.

Haka kuma, a ranar 22 ga watan nan da muke ciki, hukumar zaben tarayyar kasar Somaliya ta taba fidda wata sanarwar cewa, a halin yanzu, ana fuskantar kalubaloli da dama wajen gudanar da zabe a fannonin siyasa, kudaden gudanar da zabubbuka da kuma tsaro da dai sauransu.

Haka zalika, akasarin ra'ayoyin jama'a suna ganin cewa, mai iyuwa ne jinkirin gudanar da zaben majalisar wakilai da majalisar dattijai zai sa ba za a iya gudanar da babban zaben shugaban kasar da aka tsara gudanarwa a ran 30 ga watan Oktoba mai zuwa ba.

A ran 4 ga watan nan da muke ciki ne, fadar shugaban kasar Somaliya ta sanar da umurnin cewa, shugaban kasar mai ci Hassan Sheikh Mohamud ba zai iya gudanar da ayyukan shugaban kasa ba daga ran 10 ga watan Satumba, watau lokacin da ya kammala wa'adin aikinsa, kana, bisa umurin da ta fidda, za a iya tsawaita wa'adin aikinsa har zuwa ranar 6 ga watan Nuwamba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China