MDD, AU, EU, kungiyar raya gwamnatocin gabashin Afrika, kasashen Habasha, Italiya, Sweden, Birtaniya da Amurka sun fitar da wata haddadiyar sanarwa a jiya Lahadi a birnin Mogadishu hedkwatar kasar Somaliya, inda suka yi kira ga Somaliya da ta gudanar da zabe cikin adalci wanda zai samu amincewa daga jama'a.
Za a gudanar da zaben majalisar wakilan kasar Somaliya daga ran 24 ga watan Satumba zuwa ran 10 ga watan Oktomba na bana, kana za a gudanar da zaben majalisar dattawa daga ran 25 ga watan Satumba, sai zaben shugaban kasa wadda za a gudanar a ran 30 ga wata Oktomba. (Amina)