Bisa rahoton da 'yan sanda suka gabatar, an ce masu kai harin sun dasa wata nakiya a karkashin motar wani jami'in tsaro. Sa'an nan bayan da jami'in ya ta da mota, bom din ya fashe, wanda lamarin ya kashe jami'in nan take. Wasu jami'an tsaro 3 sun ji raunuka masu tsanani.
Har yanzu babu wanda ya dauki alhakin harin, sai dai ana tuhumar cewa kungiyar Al-Shabaab ce take da hannu cikin lamarin, ganin kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta dade tana kai irin wadannan hare-hare.
Za a gudanar da zaben majalisun kasar Somaliya a kwanaki masu zuwa, kuma kungiyar Al-Shabaab na kasancewa wata babbar barazana da kasar take fuskanta .(Bello Wang)