in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNHCR ta samar da kudi don taimakawa 'yan gudun hijirar Syria dake Sudan
2016-05-06 12:54:55 cri
Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta kasar Sudan ta tabbatar a jiya Alhamis 5 ga wata cewa, hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD wato UNHCR ta samar da kudi dala miliyan 10 don taimakawa 'yan gudun hijira na kasar Syria da suka arce zuwa kasar Sudan.

Wakilin UNHCR dake kasar Sudan Mohamed Adar ya bayyana yayin da yake ganawa da jami'an ma'aikatar harkokin gida ta Sudan da hukumar kula da 'yan gudun hijira ta kasar cewa, MDD za ta samar da gudummawar jin kai ga 'yan gudun hijira na kasar Syria fiye da dubu 80 dake kasar Sudan. Adar ya yaba wa gwamnatin kasar Sudan da tallafin ilmi da kiwon lafiya da aikin yi da ta samar wa 'yan gudun hijira na kasar Syria da ke zaune a kasar.

Sudan ita ce kasar da ta fi karbar 'yan gudun hijira na kasar Syria. 'Yan gudun hijira na kasar Syria da dama ne suke zaune a kasar ta Sudan wadda tattalin arziki da tsaronta ba su kai matsayin na kasashen Turai ba, amma duk da haka suna iya samun aikin a kasar Sudan.

Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta kasar Sudan tana ganin cewa, mai yiwuwa yawan 'yan gudun hijira daga kasar Syria da za su zo kasar Sudan zai karu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China