RDC-Congo: Shugaba Kabila ya yi kira da a kwantar da hankula
Shugaban kasar jamhuriyyar demokuradiyar Congo (RDC-Congo), Joseph Kabila, ya yi kira ga masu zanga zanga da su kwantar da hankula bayan kwanaki biyu na tashe tashen hankali a Kinshasa, babban birni kasar, wadanda suka janyo mutuwar mutane 38. Shugaba Kabila ya kuma tunatar da 'yan siyasa da dukkan kungiyoyin jama'a masu ruwa da tsaki na kasar cewa amfani da yin bore ko wasu ayyakun janyo fitina ba zasu kasance wata mafita ga shawarwarin dake gudana a yanzu ba domin warware matsalolin da suka shafi shirya sabbin zabuka kamar yadda kundin tsarin mulki da kuma wasu muhimman dokokin kasar suka tsaida. (Maman Ada)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku