in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Chadi: An bude wata cibiyar kasa ta bada jagoranci da ayyukan tabbatar da doka da oda
2016-09-22 11:18:31 cri
Ministan tsaron jama'a da shige da ficen jama'a na kasar Chadi, Ahmat Mahamat Bachir, a ranar Laraba a Djamena, babban birnin kasar, ya bude wata cibiyar kasa ta bada jagoranci kan ayyukan tabbatar da doka da oda, wanda ya kasance abu na farko a cikin wannan kasa dake fama da kalubalolin tsaro da dama, musammun ma na kungiyar Boko Haram.

A cewar mista Bachir, wannan cibiya za ta taimaka wajen tabbatar da karin hadin gwiwa da yin amfani da jami'an tsaro yadda ya kamata. Za ta taimakawa wajen kimanta dukkan matsalolin tsaro cikin lokaci a fagen daga, da daukar matakan da suka dace da kuma tattara kayayyakin da ake bukata tsakanin ofisoshin ministocin dake kula da harkokin tsaron jama'a, hukumomin gwamnati da shugabannin rundunonin abin ya shafa.

A cewar madam Mariam Mahamat Nour, ministar tattalin arziki da fasalin kasa, wannan cibiya tana wakiltar tushen tsakiyar wani matakin dake kunshe da dukkan bangarori uku na jami'an tsaron cikin gida wato 'yan sanda, jandarma da gume, a bangaren hedkwatar kasa da kuma sauran 'yankuna 23 da kasar take da su. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China