in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WFP ya kara yawan tallafin da yake bayawar a yankin tafkin Chadi
2016-08-03 09:59:12 cri
Shirin samar da abinci na duniya (WFP) yana kokarin kara yawan taimakon da ya ke bayarwa, ta yadda zai kai ga sama da mutane miliyan 1.5 da ke matukar bukatar taimako a yankin tafkin Chadi.

Kakakin MDD Stephane Dujarric wanda ya bayyana hakan a lokacin taron manema labarai, ya ce hare-haren da mayakan Boko Haram suke kaiwa kan fararen hula, su ne suka kara bukatar kayan agaji a yankin da tun farko ya ke fama da tarin matsaloli.

Ya ce, da farko shirin na WFP ya taimakawa mutane miliyan 1 da ke yankin, amma duk da haka shirin ya yana kara agajin da ya ke bayar wa, saboda karuwar mutane da suke barin muhallansu, sannan kuma yanzu ana iya shiga wasu yankunan kasar ta Najeriya ba tare da wata matsala.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China