in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
RDC-Congo: Kabila ya yi kira ga al'umma dake gabashi da su shiga sosai cikin ayyukan zabuka masu zuwa
2016-08-06 12:17:49 cri
Shugaban kasar RDC-Congo, Joseph Kabila, ya yi kira ga dukkan al'ummomin dake gundumar Nord-Kivu dake gabashin kasar da su himmatu sosai cikin ayyukan kasancewa masu zabe dake gudana, da hukumar zabe mai zaman kanta (CENI) ta kaddamar.

"Muna da wani shirin rijistan masu zabe dake gudana a dukkan fadin kasar, ina gayyatarku wajen halarta da kuma samun katin zabenku domin zabuka masu zuwa", in ji shugaban kasar Congo a yayin wani taron gangami a Kasindi, wani yankin dake kan iyaka da Uganda.

Joseph Kabila ya yi kuma kira ga al'ummar Arewacin Kivu da su runguna manufar tabbatar da zaman lafiya domin cimma nasara kan ayyukan ci gaban ababen more rayuwa da kuma maido da ikon gwamnati a wannan bangare na kasar.

Tun 'yan shekaru da dama, yankuna da kauyukan Arewacin Kivu suka kasance masu fama da hare haren 'yan tawayen Uganda na kungiyar ADF. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China