in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan adawa sun yi watsi da shiga tattaunawar sulhu a demokaradiyyar Congo
2016-07-26 10:38:41 cri
Kungiyoyin 'yan adawa a jamhuriyar demokuradiyyar Congo Kinshasa karkashin dakaru masu fafutukar kawo sauyi, sun yi fatali da shirin tattaunawar sulhu wanda kungiyar tarayyar Afrika AU ta shirya karkashin Edem Kodjo.

A wata sanarwar da shugaban kungiyar Etienne Tshisekedi ya rattabawa hannu, gamayyar kungiyoyin ta kunshi jam'iyyun adawa na jamhuriyar demokuradiyyar Congo, sun ce sun ki amincewa da wasu batutuwa, ciki har da batun da Kodjo ya sanar na kafa kwamitin da zai jagoranci shirya tattaunawar sulhun.

AU ce ta nada Kodjo a matsayin jami'in da zai jagoranci kwamitin sulhu wanda ake sa ran zai fara zamansa a ranar 30 ga watan Yulin 2016. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China