in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
OMT za ta ci gaba da taimaka wa Afrika wajen ingiza zuwan 'yan yawon bude ido
2016-09-17 12:30:01 cri

Kungiyar yawon bude ido ta duniya (OMT) ta jaddada niyyarta ta ci gaba da tallafa wa kasashen Afrika wajen kara yawan zuwan 'yan yawon bude ido a nahiyar domin ingiza bunkasuwar tattalin arziki da samar da guraben ayyukan yi a nahiyar. Elcia Grandcourt, darektar reshen Afrika na kungiyar OMT, ta bayyana a ranar jiya Jumma'a 16 ga wata a yayin wani taron kara wa juna sani na kwanaki uku dake gudana a birnin Addis-Abeba na kasar Habasha cewa, kungiyar ta OMT tana dukufa wajen taimaka wa kasashen Afrika wajen tinkarar kalubaloli a bangaren yawon bude ido, musammun ma wajen saukaka samun takardun visa, kyautata dokoki da raya ababen more rayuwar jama'a masu dacewa, da tsara manufa mai kyau. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China