in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bukaci kasashen Afirka da su koma ga aikin gona don samar da abinci
2016-09-06 20:52:47 cri
Kwararru kan shirin samar da abinci a nahiyar Afirka sun yi kira ga kasashen nahiyar da su rungumi aikin noma a wani mataki na samar da isasshen abinci da magance matsalar abinci mai gina jiki da ake fuskanta a sassa daban-pdaban na nahiyar.

Wannan kira na kunshe ne cikin wani sabon rahoto da kungiyar mai ragin inganta aikin gona a Afirka(AGRA) ta fitar yau Talata,tana mai cewa, kasashen da suka aiwatar da shirin bunkasa aikin gona a Afirka yadda ya kamata, sun samu amfani gona mai tarin yawa da samun karuwar alakaluman GDP, kana sun magance matsalar abinci mai gina jiki da suke fuskanta idan aka kwatanta da kasashen da ba su rugumi shirin ba.

Shugabar shirin na AGRA Agnes Kalibata ta bayyana a lokacin kaddamar da wannan rahoto da ya gudana a birnin Nairobin kasar Kenya cewa, a cikin shekaru goman da suka gabata, an samu ci gaba a bangaren aikin gona, lamarin da ya kasance wani mataki na samun ci gaban tattalin arziki mai dorewa wanda ya yi tasiri a dukkan bangarorin rayuwar al'umma, musamman talakawa a nahiyar Afirka.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China