in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jimilar kudin da Sin ta zuba a kasashen Afirka sun wuce dalar Amurka biliyan 100
2016-09-07 19:46:12 cri
Mataimakin daraktan hukumar raya kasa da yin kwaskwarima na kasar Sin Ning Jizhe ya bayyana cewa, hadin kan dake tsakanin Sin da kasashen Afirka cikin shekaru fiye da goma da suka wuce yana bunkasuwa cikin sauri , ya zuwa yanzu jimilar kudin da Sin ta zuba a kasashen Afirka sun wuce dalar Amurka biliyan 100, akwai kuma kamfanonin kasar Sin sama da 3100 wadanda ke gudanar da ayyukansu a nahiyar Afirka.

Darakta Ning ya bayyana haka ne a yayin da yake halartar taron dandalin tattaunawa kan zuba jari a Afirka karo na biyu da aka shirya a birnin Guangzhou na kasar Sin. Ning ya ce, kasashen Sin da Afirka suna gudanar da hadin kai ta fuskar masana'antu bisa burin neman ci gaba tare, kana ana mayar da hankali kan raya muhimman kayayyakin more rayuwar jama'a, da cin gajiyar albarkatu da makamashi ta hanyar zuba jari kai tsaye, da gudanar da kwangilar gine-gine, da hadin kan cinikayyar na'urori da fasahohi, da nufin taimakawa kasashen Afrika raya masana'antunsu, da birane da kuma harkokin sadarwa. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China