in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta tura wakilai don tattaunawa game da warware rikicin kasar Burundi
2016-06-24 12:00:55 cri
A ranar Larabar data gabata kungiyar tarayyar Afrika (AU) ta tura tawagar wakilanta zuwa Burundi domin shiga tattaunawar warware rikicin kasar wanda ya shafe shekara guda.

Lazare Makayat Safouesse, shugaban tawagar ta AU mai wakilan kasashe 15 don tabbatar da zaman lafiya, ya bayyana kyakkyawar fatar cewar za'a iya cimma nasarar warware rikicin kasar Burundin kamar yadda aka taba cimma wata yarjejeniya a shekarar 2000, wanda aka yiwa taken Arusha Agreement.

Safouesse, wanda kuma jakada ne na jamhuriya dimokaradiyyar Congo a kungiyar ta AU, ya tabbatar da hakan ne a lokacin da yake ganawa da shugaban majalisar dattawan kasar Burundin Reverien Ndikuriyo.

Mai Magana da yawun shugaban majalisar dattijan Burundin Anicet Niyongabo ya shedawa 'yan jaridu cewa, an bukaci 'yan tawagar da su nuna goyon baya ga tattaunawar sulhunta rikicin kasar ta Burundi da ke gudana.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China