in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin zai halarci babban taron MDD
2016-09-14 14:13:23 cri
Rahotanni daga kasar Sin na nuna cewa, Firaministan kasar Mr Li Keqiang zai halarci babban taron MDD karo 17, daga bisani kuma zai yi ziyarar aiki a kasashen Canada da Cuba.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ce ta bayyana hakan a nan birnin Beijing, Ta kuma bayyana cewa, Mr Li zai fara rangadin nasa ne daga ranar 18 zuwa 28 ga watan Satumba.

Babban sakataren MDD Ban Ki-moon,Firaministan kasar Canada Justin Trudeau da shugaban kasar Cuba kana jagoran majalisar ministocin kasar Raul Castro Ruz ne suka gayyaci firaminista Li Keqiang bi da bi.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China