in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Keqiang ya yi jawabi a yayin taron shugabannin kasashen Asiya da Turai karo na 11
2016-07-15 17:27:02 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya halarci taron koli na 11 na kasashen Asiya da Turai Yau da safe a birnin Ulaanbaatar, hedkwatar mulkin kasar Mongolia, inda ya ba da jawabi mai lakabi "kasashen Asiya da Turai sun hada kai don kara samun ci gaba bisa dalilin kasancewarsu kaddara bai daya".

Mr. Li Keqiang ya bayyana cewa, baya ga babban zarafin neman samun bunkasuwa da yankin Asiya da Turai ke da shi, hatta yana kuma fuskantar kalubale sosai, musamman ma a fannin ta'addanci da batun 'yan gudun hijira.

A saboda haka, ya kamata bangarorin su tabbatar da matsayi daya da aka cimma a gun taron kasashen Asiya da Turai domin girmama juna da tattauna batun cikin ruwan sanyi tare da inganta hadin gwiwa a tsakaninsu ta yadda za a daga matsayin hadin gwiwar dake tsakaninsu.

Bugu da kari, Li Keqiang ya bayyana yanayin da tattalin arzikin kasar Sin ke ciki, inda ya bayyana cewa, a farkon rabin wannan shekara, kasar Sin ta gudanar da tattalin arzikinta yadda ya kamata a lokacin da take fuskantar kalubale da dama, wannan ya yi daidai da abin da aka yi hasashe. Kasar Sin za ta ci gaba da aiwatar da gyare-gyare a cikin gida tare da bude kofa ga kassshen waje da kara gyara tsarin tattalin arzikin kasar. Sin da niyyar cimma burinta na wannan shekara a fannin tattalin arziki, domin kiyaye saurin bunkasuwarsa, ta yadda za ta ba da gundummawa ga bunkasuwar tattalin arziki da kiyaye zaman lafiya a yankin Asiya da Turai.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China