in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masana kwayoyin cutar HIV daga Afrika zasu yi taro a Namibiya
2016-09-13 10:20:42 cri
Sama da kwararru 120 daga kasashen Afrika 11 ne ake saran zasu hallara a Windhoek a gobe Laraba, domin halartar taron kwanaki 4 don gwajin kwayoyin cuta mai karya garkuwar jiki HIV.

Taron mai taken: "auna kwayoyin cutar HIV da daukar sakamakon gwajin domin inganta tsarin", kasar Amurka ce zata dauki nauyin shirin, karkashin asusun fadar shugaban kasa na tallafin gaggawa game da yaki da cutar AIDS (PEPFAR).

Hukumar lafiya ta duniya ce ta amince da gwajin kwayoyin cutar kan wasu marasa lafiya dake dauke da kwayoyin cutar, wadanda ake musu magani ta hanyar canza musu jini.

Taron bitar shine irinsa na farko da aka taba gudanarwa a kasar Namibiya.Ana saran masana cutar ta HIV zasu tattauna da kuma yin musayar ra'ayoyi game da irin dabarun da kasashen su ke amfani dasu wajen dakile yaduwar cutar.

Kasar Namibiya guda ce daga cikin kasashen Afrika 3, da suka gudanar da mafi yawan gwajin kan marasa lafiya dake dauke da kwayoyin cutar ta HIV.

Gwajin kwayoyin cutar tare da daukar matakai nada matukar muhimmanci, kuma rashin daukar matakan na iya sa mutanen da suka kamu da cutar su galabaita, ko ya yi sanadiyyar mutuwarsu.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China