in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sinawan dake zaune a Namibiya sun tallafawa 'yan Namibiya da su koyi ilmin likitanci
2015-06-21 14:20:31 cri
A ran 19 ga wata, asusun jin kai na Sinawan dake zaune a kasar Namibiya ya shirya wani bikin mika kudin yabo a Windhoek, hedkwatar kasar, inda ya tallafa wa dalibai 6 na kasar Namibiya da za su kasar Sin su koyi ilmin likitanci.

A yayin bikin, shugaban kasar Hage Geingob ya yaba wa matakin ba da kudin kyauta da Sinawa 'yan kasuwa suka dauka, kuma ya nuna godiya da yabo ga asusun jin kai na Sinawan dake zaune a kasar Namibiya. Sannan ya sa kaimi ga dalibai wadanda suka samu kudin tallafi da su yi kokarin koyon ilmi, ta yadda za su iya zama wakilai masu sada zumunta tsakanin kasashen Namibiya da Sin, kuma yana fatan su dawo Namibiya bayan da suka kammala karatunsu a kasar Sin.

Mr. Huang Yuequan, shugaban asusun jin kai na Sinawa ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu yawan daliban da suka samu kudin tallafi ya riga ya kai 34, kuma yawan kudin tallafi da asusun ya kebe ya kai kudin Sin yuan miliyan 5, wato kimanin dalar Amurka dubu dari 8. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China