A dangane da ra'ayin da firaminstan kasar Japan Shinzo Abe ya bayar game da batun tekun kudancin Sin a gun taron kolin kungiyar kasashen gabashin nahiyar Asiya, Hua Chunying ta bayyanawa 'yan jarida cewa, a yayin taron kolin gabashin nahiyar Asiya da aka kammala, firaministan kasar Sin Li Keqiang ya bayyana matsayin kasar Sin kan batun tekun kudancin kasar, kuma kasashe membobin kungiyar ASEAN sun goyi bayan wannan mataki. Yawancin kasashen sun yabawa Sin da kasashe membobin kungiyar ASEAN bisa kokarinsu na warware batun tekun kudancin Sin ta hanyar yin shawarwari, da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a tekun kudancin Sin a lokaci guda. (Zainab)