Shugaban kasar Rasha ya goyi bayan matsayin Sin kan batun tekun kudancin Sin
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya bayyana a kwanakin baya cewa, kasar Rasha tana goyon bayan matsayin kasar Sin na kin amincewa da hukuncin da aka yanke kan batun tekun kudancin kasar, a ganinta, duk wata kasar da ta tsoma baki a batun tekun kudancin Sin zai kawo cikas ga warware batun. Dangane da haka, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a yau Alhamis cewa, ra'ayin shugaba Putin ya wakilci matsayin kasa da kasa na nuna goyon baya ga adalci, kuma Sin ta nuna yabo sosai game da hakan. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku