in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban ki-moon ya yi kira da a warware batun tekun kudancin Sin ta hanyar yin shawarwari
2016-08-30 12:29:41 cri
Jiya Litinin 29 ga wata, babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya bayyana a birnin Singapore cewa, ana fatan bangarorin da batun tekun kudancin kasar Sin ya shafa za su iya warware sabanin dake tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari cikin zaman lafiya, kuma bisa ka'idojin dokokin kasa da kasa da abin ya shafa.

Mr. Ban ya bayyana haka a yayin da yake yin jawabi a jami'ar manajoji ta Singapore, a yayin da yake tsokaci kan batun da ke jawo hankalin al'umma a shiyyar, ya ce, ana nuna damuwa da yanayin tekun kudancin kasar Sin sosai, sabo da sabani da rashin fahimtar juna a tsakanin bangarori daban daban da abin ya shafa, lamarin da kuma zai iya kawo illa ga zaman lafiyar yankin.

Bugu da kari, ya ce, ya yi ta yin kira ga bangarorin da abin ya shafa su warware sabanin dake tsakninsu ta hanyar yin shawarwari kuma bisa dokokin kasa da kasa, yana kuma fatan bangarorin daban daban da batun tekun kudancin kasar Sin ya shafa za su iya kara fahimtar juna a tsakaninsu ta hanyar tsara ka'idojin tekun kudancin kasar Sin yadda ya kamata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China