in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dan kallo ya kada Neymar a lokacin da yake horo
2016-09-07 19:21:01 cri
Wani dan kallo da ya halarci horon 'yan wasan babbar kungiyar kwallon kafa ta kasar Brazil, ya kada dan wasan gaban kungiyar Neymar a yayin da 'yan wasan ke samun horo.

Lamarin dai ya afku ne a lokacin horon na musamman da 'yan wasan ke yi a gaban jama'a, wanda ya samu halartar 'yan kallo kusan 15,000 a filin wasa na Amazonia.

A lokacin da lamarin ya faru, Neymar yayi kokarin buga wata kwallo ne, sai kawai wasu gungun magoya bayan kungiyar suka kutsa kai cikin filin wasan, kana daya cikin su ya rungumi Neymar ya kuma kada shi kasa.

Dan wasaan mai shekaru 24 da haihuwa, ya kwaci kansa daga hannun mutumin cikin sauri, kana ya fice daga filin wasan cikin murna tare da abokan wasan sa.

Yanzu haka kungiyar kwallon ta Brazil tana buga wasannin share fagen shiga gasar cin kofin duniya. Kuma kungiyoyin shiyyar 4 dake kan gaba ne za su samu damar buga gasar da za a gudanar a shekarar 2018 a kasar Rasha. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China