in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalissar harkokin wajen Amurka: Ganawa a tsakanin Xi Jinping da Barack Obama ta samu nasara sosai
2016-09-07 10:03:29 cri

 

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Amurka Mark Toner, ya bayyana a jiya Talata 6 ga wata cewa, ganawar da shugaban kasar Amurka Barack Obama ya yi da takwaransa na kasar Sin Xi Jinping, kafin kaddamar da taron kolin kungiyar G20 wanda ya gudana a birnin Hangzhou na kasar Sin ta haifar da manyan nasarori.

Mr. Toner ya kuma kara da cewa, a cikin 'yan shekarun baya bayan nan, gwamnatin Obama tana kiyaye hadin kai mai karfi a kan wasu lamura. Kana kasarsa tana fatan ci gaba da inganta dangantakar abokantaka a tsakanin ta da kasar Sin.

Bugu da kari, Mr. Toner ya furta a wannan rana cewa, akwai sabani tsakanin kasashen biyu a wasu fannoni, amma duk da haka Amurka ba za ta gujewa sabanin ba, a maimakon haka, za ta ci gaba da tuntubar kasar Sin a kansu. (Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China