Djibouti za ta kafa wani kwamitin ci gaban tattalin arziki
Gwamnatin kasar Djibouti ta amince a ranar Talata da kafa wani kwamitin ci gaban tattalin arziki na Djibouti (CDED). Aiwatar da wannan hukumar shata manufofi da daukar mataki na cikin tsarin siyasar bunkasa masana'antu da kyautata yanayin harkokin tattalin arziki da shugaban kasar Djibouti, Ismail Omar Guelleh ya kirkiro. Kwamitin CDED zai kula da sanya ido kan daidaituwar ayyukan gwamnatin kasar domin bunkasa wani ci gaban tattalin arziki cikin karko. Haka kuma, makasudin shi ne samar wa gwamnati da wani makamin tsara wa da aiwatar da dubaru na siyasar tattalin arziki. (Maman Ada)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku