Gidan radiyon gwamnatin jamhuriyar ta Naijer ya rawaito cewa, an yi amana maharan 'yan kungiyar Boko Haram ne, inda suka afkawa kauyen Toumour yayin da suke haye kan rakuma a daren Jumma'ar da ta gabata. Maharan, sun kona gidaje masu yawa, sannan sun kashe jama'a da kuma jikkata wasu da dama daga cikin mazauna kauyen.
Gidan radiyon kasar ya sanar da cewa, wannan shi ne karon farko da kungiyar ta kaddamar da hari a gabashin jamhuriyar Nijer cikin watanni uku. (Ahmad Fagam)