in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yabawa kokarin gwamnatin Najeriya na tattaunawa da kungiyar Boko Haram
2016-09-01 09:16:11 cri
Kungiyar raya yankin Kubaku dake garin Chibok mai fama da rikicin Boko Haram, ta yabawa kudurin gwamnatin Najeriya na tattaunawa da mayakan kungiyar Boko Haram, a wani mataki na ganin an sako 'yan matan da ke hannun mayakan.

Wata sanarwa da kungiyar ta rabawa manema labarai a birnin Legas cibiyar kasuwancin kasar, ta ce tana fatan ikararin gwamnatin tarayyar Najeriya na sasantawa da mayakan Boko Haram zai kai ga tabbatar da fatan sake ganawar 'yan matan da iyayensu.

Sakataren kungiyar Muhammad Askira, ya yaba da rawar da sojojin Najeriya suka taka na kawar da 'yan ta'addan Boko Haram daga maboyarsu, da ma matakan shugaba Muhammadu Buhari na yaki da masu tayar da kayar baya a kasar.

Askir ya ce, suna fatan nan ba da dadewa ba 'yan matan na Chibok da ke hannun mayakan Boko Haram za su sake haduwa da iyayensu.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China