in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi kiran a hada kai domin yaki da kaifin kishin addini na matasa a Somaliya
2016-09-02 10:42:49 cri
Tawagar wanzar da zaman lafiya ta kungiyar tarayyar Afrika dake Somaliya (AMISOM) ta yi kira ga mambobin gamayyar da kuma matasa da su bada hadin kai tare da 'yan sanda domin yaki da kaifin kishin addini da kuma karfafa zaman lafiya da kwanciyar hankali a wannan kasa dake kusurwar Afrika.

Babban sufeton AMISOM, John Marete, ya bayyana a yayin wani zaman taron fadakarwa na gamayyar kan yaki da kaifin kishin addini a Beletweyne cewa ta'addanci ita ce babbar barazana ga kokarin gwamnatin Somaliya ta fuskar tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, haka kuma kare al'umommin shi ne babban nauyi na hukumomin tsaro da kuma jama'a.

Taron da 'yan sandan AMISOM suka shirya a ranar Laraba, na daga cikin jerin tarukan dake shafar fadakar da jama'a kan muhimmancin yaki da kaifin kishin addini kafin shirye shiryen zabuka masu zuwa, da zasu fara a cikin wannan watan.

Wakilan ma'aikatun gwamnati, matasa, mata da kungiyoyin fararen hula sun halarci wannan taro. Wasu kuma tarukan irin makamantan wannan zasu gudana a sauran biranen kasar.

Mataimakiyar kwamishinan 'yan sandan AMISOM, Cecilia Appiah Ampofo, ta bayyana cewa wannan taron zai baiwa matasa wata fahimta mai kyau kan mammunan tasirin kaifin kishin addini. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China