in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Boko Haram ta kashe masu gadin dabbobin Najejeriya 1900 a cikin shekaru hudu
2016-08-11 10:18:23 cri
Shugaban kungiyar masu dabbobi ta Al-Hayah a Najeriya Ibrahim Mafa a ranar Laraba ya bayyana cewa, kimanin masu gadin dabbobi 1900 a jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya, aka kashe a cikin hare hare daban daban dake mambobin kungiyar ta'addanci ta Boko suka kai a cikin shekaru hudu na baya baya.

Mista Mafa ya shedawa manema labarai a birnin Maiduguri, hedkwatar jihar Borno, cewa fiye da shanu dubu 169 da raguna da awaki dubu 63 aka rasa a lokacin wadannan hare hare daban daban.

Mista Mafa ya kara da cewa, masu gadin dabbobi sun kuma rasa gidajensu da aka kiyasta zuwa Naira biliyan 26, kimanin dalar Amurka miliyan 92 a cikin wadannan hare haren Boko Haram.

Shugaban ya kuma bayyana cewa, yankunan da suka fi fama da hare haren Boko Haram sun hada da Kala Balge, Mafa, Munguno, Bama, Konduga da Gwoza.

Najeriya ta samu cigaba a cikin yakin da take da Boko Haram a cikin shekara guda, rundunar sojojin Najeriya ta kwato yankunan kasar da dama da a lokacin baya suke hannun kungiyar Boko Haram. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China