in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata ma'ajiyar makamai ta fashe a kasar Libya
2016-06-22 13:15:36 cri
Wata ma'ajiyar makamai dake gabashin birnin Tripoli na kasar Libya ta fashe a jiya ranar 21 ga wata, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane 29 yayin da jikkata mutane fiye da 30.

Wani jami'i ya bayyana cewa, ma'ajiyar makamai da hadarin ya faru yana birnin Garaboll mai nisan kilomita 60 daga gabashin birnin Tripoli. Kafin fashewarta din, sojojin dake kula da ma'ajiyar sun yi rikici tare da fararen hula dake wurin, amma daga baya sojojin sun janye daga wannan wurin. Fararen hula dake wurin sun yi kangiya kan hanyar motoci a tsakanin Garaboll da Misrata.

Wannan jami'i ya kara da cewa, ana bincike kan dalilin fashewar bom din, an riga an kai mutane da suka ji rauni zuwa asibiti, kuma akwai yiyuwar yawan mutanen da suka mutu zai karu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China